Trend News Hausa
Siyasa

DA DUMI-DUMI: Kotu ta umarci PDP da ta gudanar da taron jam’iyyar na kasa

Wata babbar kotu a jihar Oyo ta umarci jam’iyyar PDP tare da mukaddashin shugabanta na kasa, Umar Damagum, da su ci gaba da shirye-shiryen gudanar da taron kasa na jam’iyyar da aka tsara ranar 15 ga Nuwamba a birnin Ibadan, babban birnin jihar Oyo.

Mai shari’a A.L. Akintola ne ya bayar da wannan umarni a ranar Litinin yayin da yake yanke hukunci kan wata bukatar gaggawa da Folahan Malomo Adelabi ya shigar.

Hukuncin kotun ya zo ne a daidai lokacin da ake samun rikice-rikicen cikin gida a jam’iyyar PDP kan tsarin shugabanci da kuma shirye-shiryen taron da ake sa ran zai tantance muhimman mukamai da dabarun jam’iyyar kafin zaben 2027.

Related posts

Ƴan Kwankwasiyya nada hannu a yaɗa fastocina na cewa ina neman takarar shugaban ƙasa – Ganduje

Ali Hamisu

ADC ba za ta lamunci kakaba ‘yan takara ko cin amanar jam’iyya ba – David Mark

Ali Hamisu

2027: ‘Yan Najeriya da kansu za su roki Tinubu ya ci gaba da mulki har zuwa 2031 – Jigo a jam’iyyar APC

Ali Hamisu

Leave a Comment