Tsohon shugaban ƙasa Olusegun Obasanjo ya yi watsi da ikirarin cewa ya taɓa neman wa’adi na uku a ofis, inda ya jaddada cewa ba shi da wannan buri a lokacin mulkinsa.
A yayin jawabi a ranar Laraba, a taron tattaunawar dimokuraɗiyya da Gidauniyar Goodluck Jonathan ta shirya a birnin Accra, Obasanjo ya ce babu wani ɗan Najeriya – mai rai ko wanda ya rasu – da zai iya tabbatar da cewa ya taɓa faɗa masa yana neman wa’adi na uku.
“Ina da hankali. Da na so wa’adi na uku, na san hanyar da zan bi wajen samunsa. Kuma babu wani ɗan Najeriya, mai rai ko mamaci, da zai ce na kira shi na faɗa masa ina son wa’adi na uku,” in ji Obasanjo.
Ya kuma jaddada cewa ya riga ya cimma manyan abubuwa masu wahala, inda ya kawo misali da samun rangwamen bashi ga Najeriya a lokacin mulkinsa, wanda ya ce ya fi wahalar samu fiye da wa’adi na uku.
“Ina ta gaya musu cewa, ku duba, da na so samun rangwamen bashi wanda ya fi wahalar samu fiye da wa’adi na uku, na samu shi. To da na so wa’adi na uku, da na samu shi ma,” in ji shi.
